Skip to content
Ayuba 41:1-11

Ayuba 41:1-11

1
“Ko za ka iya kama dodon ruwa da ƙugiyar kamar kifi ko kuma ka daure harshenta da igiya?
2
Za ka iya sa igiya a cikin hancinta ko kuma ka huda muƙamuƙanta da ƙugiya?
3
Za tă ci gaba da roƙonka ka yi mata jinƙai? Ko za tă yi maka magana a hankali?
4
Za tă yi yarjejjeniya da kai don ka ɗauke ta tă zama baiwa gare ka dukan kwanakin ranta?
5
Za ka yi wasa da ita kamar yadda za ka yi da tsuntsu? Ko za ka daure ta da tsirkiya domin bayinka mata?
6
’Yan kasuwa za su saye ta ko za su raba ta a tsakaninsu?
7
Ko za ka iya huda fatarta da kibiya ka kuma huda kansa da māsu?
8
In ka ɗora hannunka sau ɗaya a kanta za ka tuna da yaƙin da ba za ka sāke yi ba!
9
Duk ƙoƙarin kama ta banza ne; ganin ta kawai abin tsoro ne.
10
Ba wanda ya isa yă tsokane ta. Wane ne kuma ya isa yă yi tsayayya da ni?
11
Wane ne yake bi na bashi da dole in biya? Duk abin da yake ƙarƙashin sama nawa ne.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options