Skip to content
Ayuba 37:6-13

Ayuba 37:6-13

6
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options