Ayuba 37:14-20
14
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
Settings