Skip to content
Ayuba 37:1-5

Ayuba 37:1-5

1
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options