Tsallake zuwa abun ciki
Ayuba 34:16-30

Mulkin Allah marar son kai da adalci

Ayuba 34:16-30
16
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19
wanda ba ya nuna sonkai ga ’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options