Ayuba 30:1-5
1
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
Settings