Skip to content
Ayuba 21:7-13

Ayuba 21:7-13

7
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8
Suna ganin ’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11
Suna aika ’ya’yansu kamar garke; ’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options