Skip to content
Ayuba 21:17-22

Ayuba 21:17-22

17
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19
An ce ‘Allah yana tara wa ’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options