Skip to content
Ayuba 21:7-16

Ayuba 21:7-16

7
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8
Suna ganin ’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11
Suna aika ’ya’yansu kamar garke; ’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama.
14
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options