Skip to content
Ayuba 21:1-6

Ayuba ya roƙi a saurare shi da kyau

Ayuba 21:1-6
1
Sai Ayuba ya amsa,
2
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Settings

Reading style

Typeface

Font size 19px

Reading width 90 chars

Options