Skip to content
Ayuba 21:27-34

Ayuba 21:27-34

27
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options