Skip to content
Ayuba 19:13-22

Ayuba 19:13-22

13
“Ya raba ni da ’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17
Numfashina yana ɓata wa matata rai; ’yan’uwana sun ƙi ni.
18
Har ’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options