Ayuba 19:23-27
23
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
Settings