Skip to content
Ayuba 14:1-12

Ayuba 14:1-12

1
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
7
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
8
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
9
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
10
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
11
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
12
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options