Ayuba 14:1-6
1
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
Settings