Skip to content
Ayuba 14:1-6

Ayuba 14:1-6

1
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options