Skip to content
Irmiya 49:23-27

Hukunci a kan Dimashƙu

Irmiya 49:23-27
23
Game da Damaskus. “Hamat da Arfad sun giggice, gama sun ji mummunar labari. Suna damuwa, sun damu kamar tekun da baya hutu.
24
Damaskus ta karai ta juya don ta gudu tsoro kuma ya kama ta; wahala da zafi sun kama ta, zafi kamar na mace mai naƙuda.
25
Me ya sa ba a tafi aka bar sanannen birnin nan ba, birnin da nake jin daɗi?
26
Tabbatacce, samarinta za su fāɗi a tituna; dukan sojojinta za su yi shiru a wannan rana,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
27
“Zan cinna wa katangar Damaskus wuta; za tă ci kagaran Ben-Hadad.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options