Tsallake zuwa abun ciki
Farawa 22:20-24

Zuriyar Nahor

Farawa 22:20-24
20
Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka, ’ya’ya maza;
21
ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
22
Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
23
Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan ’ya’ya maza takwas.
24
Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa ’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options