Tsallake zuwa abun ciki
Farawa 22:15-19

An tabbatar da alkawari da rantsuwa

Farawa 22:15-19
15
Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
16
ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
17
tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
18
ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
19
Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options