Tsallake zuwa abun ciki
2 Sama’ila 15:7-10

2 Sama’ila 15:7-10

7
A ƙarshen shekara huɗu, Absalom ya ce wa sarki, “Bari in tafi Hebron in cika alkawarin da na yi wa Ubangiji.
8
Yayinda bawanka yake zama a Geshur, a Aram, na yi wannan alkawari, na ce, ‘In Ubangiji ya komo da ni Urushalima, zan yi wa Ubangiji sujada a Hebron.’ ”
9
Sarki ya ce, “Ka sauka lafiya.” Sai ya tafi Hebron.
10
Sai Absalom ya aiki manzanni a asirce cikin dukan kabilan Isra’ila, ya ce musu su ce, “Da zarar kuka ji an busa ƙaho, sai ku ce, ‘Absalom sarki ne a Hebron.’ ”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options