Skip to content
2 Korintiyawa 10:1-6

2 Korintiyawa 10:1-6

1
Ni Bulus da kaina, ina roƙonku albarkacin tawali’u da sanyin hali na Kiristi, ni da ake yi wa kirari “marar tsanani” a cikinku, amma “mai matsawa” sa’ad da nake rabe da ku!
2
Ina roƙonku cewa sa’ad da na zo kada ku tilasta ni in matsa muku, gama na tabbata zan iya tsaya wa waɗanda suka ce abin da muke yi sha’anin duniya ne.
3
Ko da yake muna cikin duniya, ba ma yaƙi kamar yadda duniya take yi.
4
Makaman da muke yaƙi da su, ba makamai na duniya ba ne. Sai dai na ikon Allah ne, masu rushe wuraren mafaka masu ƙarfi.
5
Muna ka da masu gardama da kowane tunanin ɗaga kai da yake kafa kansa gāba da sanin Allah, muna kuma jan hankalin kowa ga bautar Kiristi.
6
A shirye muke mu hori kowane rashin biyayya, sa’ad da biyayyarku ta cika.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options