Tsallake zuwa abun ciki
1 Sama’ila 19:11-14

1 Sama’ila 19:11-14

11
Shawulu ya aiki mutane zuwa gidan Dawuda su yi gadin gidan, su kuma kashe Dawuda. Amma Mikal matar Dawuda ta gargaɗe Dawuda, ta ce, “In ba ka gudu a daren nan ba, kashegari za a kashe ka.”
12
Haka kuwa Mikal ta sauko da Dawuda ta taga ya gudu, ya tsere.
13
Sai Mikal ta ɗauki gunki ta kwantar da shi a gādo, ta sa masa gashin akuya a kansa, sai ta rufe da mayafi.
14
Da Shawulu ya aiki mutane su kama Dawuda. Mikal ta ce, “Ba shi da lafiya.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options