Tsallake zuwa abun ciki
1 Korintiyawa 16:19-24

Gaisuwa da albarkar ƙarshe

1 Korintiyawa 16:19-24
19
Ikkilisiyoyin da suke a lardin Asiya suna gaisuwa. Akwila da Firiskila suna gaishe ku sosai cikin Ubangiji, haka ma ikkilisiyar da takan taru a gidansu.
20
Dukan ’yan’uwa a nan suna gaisuwa. Ku gai da juna da sumba mai tsarki.
21
Ni, Bulus nake rubuta wannan gaisuwa da hannuna.
22
Duk wanda ba ya ƙaunar Ubangiji, la’ana ta zauna a kansa. Zo, ya Ubangiji!
23
Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da ku.
24
Ina gaishe ku duka, gaisuwar ƙaunata cikin Kiristi Yesu. Amin.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options