Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da The Fall of Man

13 ayoyi · 34 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

  1. To, maciji dai ya fi kowane a cikin namun jejin da Ubangiji Allah ya yi wayo. Ya ce wa macen, “Tabbatacce ne Allah ya ce, ‘Kada ku ci daga kowane itace a lambu’?”

  2. Macen ta ce wa macijin, “Za mu iya ci daga ’ya’ya itatuwa a lambun,

  3. amma Allah ya ce, ‘Kada ku ci daga ’ya’yan itacen da yake tsakiyar lambu, kada kuma ku taɓa shi, in ba haka ba kuwa za ku mutu.’ ”

  4. Maciji ya ce wa macen, “Tabbatacce ba za ku mutu ba.

  5. Gama Allah ya san cewa sa’ad da kuka ci daga itacen idanunku za su buɗe, za ku kuma zama kamar Allah, ku san abin da yake mai kyau da abin da yake mugu.”

  6. Duk sun kauce gaba ɗaya, sun zama marasa amfani; babu wani mai aikata nagarta, babu ko ɗaya.”

  7. “Maƙogwaronsu kamar buɗaɗɗun kaburbura ne, harsunansu suna yin ƙarya.” “Dafin mugun maciji yana a leɓunansu.”

  8. “Bakunansu sun cike da la’ana da ɗacin rai.”

  9. “Ƙafafunsu suna saurin kai su zuwa ga zub da jini;

  10. hallaka da baƙin ciki suna ko’ina a hanyoyinsu,

  11. Waɗanda suke rayuwa bisa ga mutuntaka sun kafa hankulansu a kan sha’awace-shawa’acen jiki; amma waɗanda suke rayuwa bisa ga Ruhu sun kafa hankulansu a kan abubuwan da Ruhu yake so.

  12. Ƙwallafa rai ga al’amuran halin mutuntaka ƙarshensa mutuwa ne, ƙwallafa rai ga al’amuran Ruhu kuwa rai ne da salama;

  13. hankalin mai zunubi na gāba da Allah. Ba ya biyayya da dokar Allah, ba kuwa zai iya yin haka ba.