Skip to content
Romawa 15:30-33

Romawa 15:30-33

30
Ina roƙonku ’yan’uwa, saboda Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma saboda ƙaunar Ruhu, ku haɗa kai tare da ni cikin famata ta wurin yin addu’a ga Allah saboda ni.
31
Ku yi addu’a don in kuɓuta daga hannun marasa bi a Yahudiya don kuma gudummawar da nake kaiwa Urushalima ta zama abar karɓa ga tsarkaka a can,
32
don da yardar Allah, in iso wurinku da farin ciki in kuma wartsake tare da ku.
33
Allah na salama yă kasance tare da ku duka. Amin.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options