Zabura 83:4-8
4
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. Sela
Settings