Skip to content
Zabura 8:3-9

Zabura 8:3-9

3
Sa’ad da na dubi sammai, aikin yatsotsinka, wata da taurari waɗanda ka ajiye a wurarensu,
4
wane ne mutum da kake tunawa da shi, ɗan mutum da kake lura da shi?
5
Ka yi shi ƙasa kaɗan da Allah ka yi masa rawani da ɗaukaka da girma.
6
Ka mai da shi mai mulki bisa ayyukan hannuwanka; ka sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa,
7
dukan shanu da tumaki, da kuma namun jeji,
8
tsuntsayen sararin sama da kifin teku, da dukan abin da yake yawo a ƙarƙashin ruwan teku.
9
Ya Ubangiji, shugabanmu, sunanka da girma take a cikin dukan duniya!
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options