Rukia maudhui
Zabura 78:17-28

Zabura 78:17-28

17
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options