Zabura 78:12-16
12
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Settings