Zabura 77:2-9
2
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. Sela
4
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” Sela
Settings