Skip to content
Zabura 77:5-9

Zabura 77:5-9

5
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” Sela
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options