Zabura 77:10-15
10
Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
11
Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
12
Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
13
Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
14
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. Sela
Settings