Zabura 66:13-20
13
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. Sela
16
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Settings