Skip to content
Zabura 66:8-12

Zabura 66:8-12

8
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options