Tsallake zuwa abun ciki
Zabura 52:1-4

An hukunta mugun mai taƙama

Zabura 52:1-4
1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Doyeg mutumin Edom ya tafi wurin Shawulu ya ce masa, “Dawuda ya tafi gidan Ahimelek.” Me ya sa kake fariya game da mugunta, kai babban mutum? Me ya sa kake fariya dukan yini, kai da kake abin kunya a idanun Allah?
2
Harshenka kan shirya hallaka; yana nan kamar reza mai ci, kana ta ruɗu.
3
Kana ƙaunar mugunta fiye da alheri, ƙarya a maimakon faɗin gaskiya. Sela
4
Kana ƙaunar kowace kalmar cutarwa, Ya kai harshe mai ruɗu!
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options