Zabura 50:9-14
9
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Settings