Zabura 50:7-11
7
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
Settings