Zabura 46:4-6
4
Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
5
Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
6
Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.