Zabura 137:3-6
3
gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
4
Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
5
In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
6
Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
Settings