Skip to content
Karin Magana 5:1-14

Karin Magana 5:1-14

1
Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
2
don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
3
Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
4
amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
5
Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari.
6
Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
7
Yanzu fa, ’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
8
Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
9
don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
10
don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
11
A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
12
Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
13
Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
14
Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options