Karin Magana 4:20-27
20
Ɗana, ka kula da abin da nake faɗa, ka saurara sosai ga kalmomina.
21
Kada ka bari su rabu da kai, ka kiyaye su a cikin zuciyarka;
22
gama rai ne ga waɗanda suke nemansu da kuma lafiya ga dukan jikin mutum.
23
Fiye da kome duka, ka tsare zuciyarka, gama maɓulɓulan ruwan rijiyar rai ne.
24
Ka kau da muguwar magana daga bakinka; ka yi nesa da magana marar kyau daga leɓunanka.
25
Bari idanunka su dubi gaba sosai, ka kafa idanunka kai tsaye a gabanka.
26
Ka san inda ƙafafunka suke takawa ka bi hanyoyin da suke daram kawai.
27
Kada ka kauce dama ko hagu; ka kiyaye ƙafarka daga mugunta.
Settings