Karin Magana 22:17-34
17
Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
18
gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
19
Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
20
Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
21
ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
22
Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
23
gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
24
Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
25
in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
26
Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
27
gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
28
Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
29
Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
Settings