Skip to content
Ƙidaya 32:33-38

Ƙidaya 32:33-38

33
Sai Musa ya ba wa mutanen Gad, mutanen Ruben, da rabin mutanen Manasse ɗan Yusuf, masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da masarautar Og na Bashan, dukan ƙasar, tare da biranenta da kuma yankunan da suke kewaye.
34
Mutanen Gad suka gina Dibon, Atarot, Arower,
35
Atrot Shofan, Yazer, Yogbeha,
36
Bet-Nimra, da Bet-Haran a matsayin birane masu katanga, suka kuma gina katanga don dabbobinsu.
37
Mutanen Ruben suka sāke gina Heshbon, Eleyale, da Kiriyatayim,
38
haka kuma suka gina Nebo da Ba’al-Meyon (an canja waɗannan sunaye) suka kuma gina Sibma. Suka ba wa biranen da suka sāke ginawa sunaye.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options