Tsallake zuwa abun ciki
Ƙidaya 24:20-25

Maganganu a kan al’ummai

Ƙidaya 24:20-25
20
Sai Bala’am ya ga Amalek, ya kuma furta maganarsa. “Amalek yana cikin al’ummai na fari, amma zai zama na ƙarshen da za a hallaka.”
21
Sai ya ga Keniyawa, ya kuma furta maganarsa. “Wurin zamanku lafiya yake, an kuma sa sheƙarku a cikin duwatsu;
22
duk da haka, za a hallaka ku Keniyawa sa’ad da Asshur ya kame ku.”
23
Sai ya furta maganarsa ya ce, “Wayyo, wa zai rayu sa’ad da Allah ya yi haka?
24
Jiragen ruwa za su zo daga Kittim; za su murƙushe Asshur da Eber, amma su ma za a hallaka su.”
25
Sa’an nan Bala’am ya tashi ya koma gidan, Balak kuma ya yi tafiyarsa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options