Skip to content
Mattiyu 24:4-11

Mattiyu 24:4-11

Alamun farkon wahaloli

4
Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
5
Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
6
Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
7
Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
8
Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
9
“Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
10
A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
11
annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.

Duba kuma

Sauran wuraren da Nassi ya faɗi haka

  • Yohanna 16:2

    Za su kore ku daga majami’a; lalle, lokaci yana zuwa da duk wanda ya kashe ku, zai ɗauka yana yin wa Allah hidima ne.
    daga aya ta 9
  • Yohanna 15:19

    Da ku na duniya ne, da ta ƙaunaci abinta. Kamar yadda yake, ku ba na duniya ba ne, na zaɓe ku daga duniya, shi ya sa duniya take ƙinku.
    daga aya ta 9
  • Yohanna 15:20

    Ku tuna da kalmomin da na yi muku cewa, ‘Ba bawan da ya fi maigidansa,’In sun tsananta mini, ku ma za su tsananta muku. Da sun yi biyayya da koyarwata, da za su yi biyayya da taku ma.
    daga aya ta 9
  • Markus 13:7

    Sa’ad da kuka ji labarun yaƙe-yaƙe da jita-jitar yaƙe-yaƙe, kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru. Amma ƙarshen tukuna.
    daga aya ta 6
  • Markus 13:8

    Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki kuma yă tasar wa mulki. Za a yi girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam, a kuma yi yunwa. Waɗannan dai mafarin azabar naƙuda.
    daga aya ta 6
  • Luka 21:16

    Har iyayenku, da ’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
    daga aya ta 9
  • Luka 21:17

    Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
    daga aya ta 9
  • Ru’uya ta Yohanna 2:10

    Kada ka ji tsoron wahalar da kake gab da sha. Ina gaya maka, Iblis zai sa waɗansunku a kurkuku don yă gwada ku. Za ku sha tsanani na kwana goma. Ka yi aminci ko da za a kashe ka, ni kuwa zan ba ka rawanin rai.
    daga aya ta 9
  • Luka 21:11

    Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
    daga aya ta 7
  • Luka 21:9

    Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
    daga aya ta 6
  • Mattiyu 24:11

    annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
    daga aya ta 5
  • Mattiyu 24:24

    Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
    daga aya ta 5

Inda wannan ya faru

All Matthew Sites (Jerusalem)
All Matthew Sites (Jerusalem) View full PDF
The Last Week of Jesus' Life (With Reference Table)
The Last Week of Jesus' Life (With Reference Table) View full PDF
The Last Week of Jesus' Life (Map Only)
The Last Week of Jesus' Life (Map Only) View full PDF

Map © Biblica Open Bible Maps · CC BY-SA 4.0

Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options