Tsallake zuwa abun ciki
Mattiyu 10:1-4

Yesu ya ba manzanni goma sha biyu aiki

Mattiyu 10:1-4
1
Sai ya kira almajiransa goma sha biyu wurinsa ya kuma ba su iko su fitar aljanu, su kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.
2
Ga sunayen manzannin nan goma sha biyu, da fari, Siman (wanda ake kira Bitrus) da ɗan’uwansa Andarawus; Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna;
3
Filibus da Bartolomeyu; Toma da Mattiyu mai karɓar haraji; Yaƙub ɗan Alfayus da Taddayus;
4
Siman Zilot da kuma Yahuda Iskariyot wanda ya bashe Yesu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options