Tsallake zuwa abun ciki
Markus 15:16-20

Ba’a da Sarkin

Markus 15:16-20
16
Sojojin suka tafi da Yesu cikin fadar gwamna (wato, Firetoriyum), suka kira dukan kamfanin sojoji wuri ɗaya.
17
Suka sa masa wata riga mai ruwan shunayya, suka kuma tuƙa rawanin ƙaya suka sa masa.
18
Sai suka fara ce masa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
19
Suka dinga bugunsa a kā da sanda, suka tattofa masa miyau. Suka durƙusa suka yi masa bangirma na ba’a.
20
Bayan da suka gama yin masa ba’a, suka tuɓe rigar mai ruwan shunayyar, suka sa masa nasa tufafi. Sai suka tafi da shi don a gicciye shi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options