Tsallake zuwa abun ciki
Markus 14:22-26

Kafa Jibin Ubangiji

Markus 14:22-26
22
Yayinda suke cin abinci, sai Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya, ya ba wa almajiransa, yana cewa, “Ku karɓa, wannan jikina ne.”
23
Sai kuma ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, ya kuma miƙa musu, dukansu suka sha daga ciki.
24
Sai ya ce musu, “Wannan jinina ne na alkawari, wanda aka zubar da shi saboda mutane da yawa.
25
Gaskiya nake gaya muku, ‘Ba zan ƙara sha daga ’ya’yan inabi ba, sai ranan nan, da zan sha shi sabo a mulkin Allah.’ ”
26
Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options