Zum Inhalt springen
Markus 1:29-34

Markus 1:29-34

29
Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
30
Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31
Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
32
A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
33
Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
34
Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options