Skip to content
Luka 20:27-33

Luka 20:27-33

27
Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
28
“Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba ’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa ’ya’ya.’
29
To, an yi waɗansu ’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba ’ya’ya.
30
Na biyun,
31
da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu ’ya’ya.
32
A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
33
Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options