41
Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
42
Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
43
sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.” ’
44
Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”